1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Karuwar annobar kwalara a Yemen

July 22, 2017

Hukumar lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya tare da wasu kungiyoyin agaji sun sake yin kashedi dangane da yaduwar da annobar kwalara ke ci gaba da yi a kasar Yemen.

https://p.dw.com/p/2h0i5
Jemen Cholera
Hoto: Reuters/A.Zeyad

A cewar hukumar, matsalar ka iya zarta wadda ta faru a kasar Haiti da ke matsayi mafi muni tun a shekara ta 2010. Ta ce babu alamun shawo kan annobar ya zuwa yanzu, musamman ma yadda damina ke kara ta'azzara lamarin, a cewar mai magana da yawun MDD a Yemen din, Farhan Haq.

Ita ma kungiyar agaji ta OXFAM wadda ke da cibiya a Birtaniya, ta ce wannan shi ne yanayi mafi muni da aka taba gani a tsukin shekara guda. Sama da mutum dubu da 800 ne dai cutar ta halaka yayin da wasu dubu 370 kuwa suka kamu, daga watan Afrilun zuwa wannan lokacin.