1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasashen Duniya na ganawa a Amirka

September 19, 2016

Ana sa ran shuwagabannin kasashen duniya za su tabka mahawara a zauren Majalisar Dinkin Duniya kan rashin tsaro a Siriya da batun tattalin arziki.

https://p.dw.com/p/1K4fq
New York UN Gipfel Rede Obama
Hoto: Reuters/M. Segar

A taron dai ana sa ran cewar Babban sakataren MDD Ban Ki Moon wanda zai ajiye mukaminsa a ranar 31 ga watan Disamba da shugaba Barack Obama na Amirka da ke kammala wa'adin mulkinsa a watan Janairu, za su yi jawabinsu na karshe a gaban majalisar a yayin da firaministan Birtaniya Theresa May za ta yi fitowarta ta farko tun bayan dare kujera mulki a kasa da watanni uku da suka gabata bayan ficewar kasarta daga Kungiyar tarayyar Turai EU.