Kashedi ga Najeriya kan batun tsaro
November 23, 2014Zabubukan shekara mai zuwa ta 2015 na ci gaba da karatowa a Tarayyar Najeriya, yayin da ake ci gaba da samu tada jijiyoyin wuya tsakanin 'yan siyasa da ma tabarbarewar batun tsaro a wannan kasa.
Kashedin na International Crisis Group da ya fito a cikin wani rahoton da ta fitar mai shafi 42, na zuwa ne bayan wani hargitsi da aka fuskanta a majalisar wakilan kasar, bayan da jami'an tsaro na 'yan sanda suka yi amfani da borkonon tsofuwa a daidai lokacin isowar kakakin majalisar wakilan kasar, inda ake ganin iri-irin wannan yanayi ba zai haifar da da mai ido ba, inda wannan kungiya ta kara da cewa muddin dai ana so a kauce wa zubar da jini, to ala tilas sai an gaggauta samar da cikakken tsarin zabe da ma samar da cikakken tsaro ga zaben.
Mawallafi: Salissou Boukari
Edita : Umaru Aliyu