1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kiran gurfanar da Assad gaban kotu

November 10, 2012

Tsohon mai gabatar da ƙara a kotun hukuntan laifukan yaƙi ta ICC Luis Moreno-Ocampo ya ce akwai shaidun da ake buƙata na gurfanar da shugaba Bashar Al-Assad na Siriya a kotu.

https://p.dw.com/p/16gQi
GettyImages 98099063 Syrian President Bashar al-Assad attends the closing session of the Arab League Summit in the Libyan coastal city of Sirte on March 28, 2010. Arab leaders met behind closed doors to thrash out a united strategy against Israel's settlement policy as the Jewish state accused them of lacking moderation and blocking peace efforts. AFP PHOTO/JOSEPH EID (Photo credit should read JOSEPH EID/AFP/Getty Images)
Bashar al-AssadHoto: AFP/Getty Images

Luis Moreno Ocampo ya ambata hakan ne yayin wata hira da kafar watsa labaran Canada ta CBC ta yi da shi a jiya Juma'a inda ya ce hakan ya zama wajibi saboda irin ɗumbin laifukan yaƙin da ya ce dakarun da ke biyayya ga shugaba Assad ke tafkawa a cikin ƙasar a yaƙin da su ke yi da masu rajin kawo sauyi.

Tsohon mai gabatar da ƙarar ta ICC ya ce ɗaukar wannan mataki na kame Assad ɗin bisa la'akari da yadda ake kisan fararen hula a ƙasar ita ce hanya ɗaya tilo da za a bi wajen kawar da ricikin da ƙasar fama da shi tun cikin watan Maris ɗin shekarar da ta gabata.

To sai dai yayin da Mr. Ocampo ke waɗannan kalamai, a hannu guda kuma ya ce baya goyon bayan yin amfani da tsinin bindiga wajen kawar da Assad daga karagar mulki domin kuwa hakan ba hanya ba ce mai ɓullewa.

Mawallafi : Ahmed Salisu
Edita : Halima Balaraba Abbas