1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kiristocin ƙasashen Larabawa na fiskantar barazana

Usman ShehuOctober 30, 2013

Rikicin da ke faru a Gabas Ta Tsakiya ya saka Kiristocin yankin a wani halin fargaba da rashin tabbas, inda ake ta kai musu hare-hare

https://p.dw.com/p/1A8Mb
Pope Tawadros II (C), the 118th Pope of the Coptic Orthodox Church of Alexandria and Patriarch of the See of St. Mark, leads the Coptic Christmas Eve Mass at St. Mark Cathedral, in Cairo January 6, 2013. REUTERS/Mohamed Abd El Ghany (EGYPT - Tags: RELIGION ANNIVERSARY)
Bikin Ƙiɗawan MasarHoto: Reuters

Boren neman sauyi da a yanzu haka ke ci gaba da faruwa a ƙasashen Larabawa, ya haddasa barazana ga rayuwar Kiristoci da ke yankin. Tashe-tashen hankula na siyasa da suke faruwa a yankin, suna ƙarawa ƙungiyoyi masu kaifin kishin addinin Islama ƙarfi, yayin da su kuwa Kiristoci wasunsu ke tserewa daga ƙasashensu na asali. Bisa waɗannan dalilan ya sa majalisar Kiristoci a yankin ta ke son nunawa 'yan uwansu dama duniya, irin wannan matsalar da suka samu kansu.

A cikin shekaru ukun da suka gabata dai, Kiristoci da dama a yankin Gabas Ta Tsakiya suka shiga wannan yanayi mawuyaci a rayuwarsu, sakamakon guguwar neman sauyi da ta kaɗa a yankin. Habib Badr, shi ne Father da ke kula da Mujami'ar Evangelika da ke a birnin Beirut na Lebanon, wanda a yanzu yake cikin babbar damuwa, kan halin da Kiristoci suka shiga a yankin.

A picture taken on August 14, 2013, shows the facade of the Prince Tadros Coptic church after being torched by unknown assailants in the central Egyptian city of Minya. Egypt's Christians are living in fear after a string of attacks against churches, businesses and homes they say were carried out by angry supporters of ousted Islamist president Mohamed Morsi. AFP PHOTO/STR (Photo credit should read -/AFP/Getty Images)
Wata mujami'a da aka ƙona a MasarHoto: AFP/Getty Images

"Guguwar neman sauyin ta baiwa ƙungiyoyi masu kaifin kishin Islama ƙarfi. Lamarin ya sauya tinanin kowa, walau Musulmi ko Kirista da dai sauransu. Idan dai suka ƙi ba da hadin kai, imma dai a ci zarafinsu ko kuma a hallaka su. A nan mu kiristoci a Gabas Ta Tsakiya tsiraru ne, don haka mu aka fi gallazawa. A yanzu muna tserewa daga ƙasashenmu na asali"

Dama can dai Kiristocin sun hangi irin wannan matsalar tun fara bore a yankin. Don haka ne ma a bara suka kafa wata majalisa da suka kira (Assambly of Eastern Christians) inda suke taruwa don tattauna matsalolinsu, kana su kan karɓi rahotanni daga sassan, domin jin halinda ake ciki. Fuad Abu Nader, mamba ne a majalisar daga ƙasar Lebanon.

Archbishop Touma Iramia Gewargis, head of the Nineveh and Duhuk diocese in Iraq, speaks to Iraqi Chaldean-Assyrians who crowd the church to mark the 71st anniversay of the "Chaldean-Assyrian Martyr Day' at the Ibrahim Al-Khalil Church on the outskirts of Damascus, Sunday, 08 August 2004, a week after five churches in Iraq were bombed. The church bombings killed some 11 people and wounded more than 50 others. The ceremonies were held to mark a 1933 massacre against Chaldean-Assyrians demanding ethnic rights. More than 5,000 Christians were killed during the massacres the Chaldean-Assyrians commemorate annually 07 August. Foto: Youssef Badawi epa dpa
Kiristocin SiriyaHoto: picture-alliance/dpa

Ya ce "Muna son mu hada kai, mu kuma nuna addinin da muke bi na Kirista. Ganin yanayin da aka shiga a Gabas Ta Tsakiya, bai kamata mu tsaya muna magana kan mujami'ar da mutum yake bi. Don haka so muke mu riga magana da murya guda"

Wannan majalisar Kiristocin dai an kafa ta ne tun a tsakiyar shekarun 1970, amma saboda matsalar cikin gida da ta fuskanta, majalisar ba ta yi wani tasiri ba. Sai dai a yanzu ganin halin da aka shiga a yankin, Abu Nader ya ce, ya zama wajibi su nemi wata murya guda da za ta kare muradunsu. Shi kuwa Habib Badr, ya ce akwai buƙatar majalisar ta nemi hadin kai da Musulmai.

ARCHIV - Eine maronitische Kirche (vorne) und eine islamische Moschee, aufgenommen in der syrischen Stadt Maalula (Archivfoto vom 26.10.2005). Das Dorf Maalula ist die einzige Stadt in Syrien mit einer christlichen Mehrheit in der Bevölkerung. Im Libanon, in Syrien und in Jordanien, wo arabische Katholiken, Protestanten und Orthodoxe leben, ist es relativ einfach, eine Bewilligung für den Bau einer Kirche zu erhalten. Mit Abstand am schwierigsten ist die Lage im islamischen Königreich Saudi-Arabien, wo es keine einheimischen Christen gibt und der Bau von Kirchen strikt verboten ist. Foto: Oliver Berg (zu dpa-Korr. "Kirchenerbauer haben es in der arabischen Welt nicht immer leicht" vom 03.06.2007) +++(c) dpa - Bildfunk+++
Mujami'a da Masallaci a haɗe a SiriyaHoto: picture-alliance/dpa

"Dole ne mu haɗa kai da Musulmai, domin su shawo kan masu tsattsauran ra'ayi da ke cikinsu. Domin su ma suna daga cikin wadanda wannan lamarin ya shafa. Don haka ya zama wajibi a buɗe wata ƙofar tattaunawa da 'yan Sunni, waɗanda su ne suka fi yawa a yankin"

A Gabas Ta Tsakiya dai an yi kiyasin cewa Kiristoci sun kai kashi 10 cikin ɗari na al'ummar yankin. Kiristocin da suka fi yin fice su ne Ƙibɗawa a ƙasar Masar, sai kuma na Siriya ke bi a baya. A ƙasar Lebanon akwai Kiristoci da dama da ke riƙe da muƙaman gwamnati. A ƙasar Masar kimanin mujami'u 43 da gidajen Krisitoci 200, masu kaifin kishin addini suka kai wa hari, tun fara tarzumar siyasa a ƙasar. Yanzu haka a ƙasar Iraƙi bai fi ɗaya bisa biyar na Kiristocin ƙasar ke zama a ciki ba, inda suka tsere sakamkon hare-haren da ake kai musu, tun bayan kifar da gwamnatin Marigayi Saddam Hussein a shekara ta 2003.


Mawallafa: Mona Naggar / Usman Shehu Usman

Edita: Umaru Aliyu