Kisa mafi muni a tarihin Boko Haram
January 9, 2015Masu tserewa daga garin na Baga suka ce darururuwan mutane da ba za su kirgu ba sun kwanta dama a harin, musamman ma kananan yara da mata da tsofaffin da ba zasu iya gudu ba. kungiyar ta Boko Haram ta kwaci sansanin soja da ke kusa da iyakar Najeriya da hCadi, bayan da mayakan suka shiga garin a ranar uku ga watan Janairu su na harba makaman roka da gurneti.
Rahoton da kungiyar ta Amnesty ta fitar a ranar Jumma'a, ya nunar da cewa kusan garin an konesh: Sannan kusan mutane 2,000 an kashe, wani abu da ke nuna yadda hare-haren kungiyar ke ci gaba da lakume rayukan fararen hula.
Shekaru biyar na ayyukan Boko Haram yayi sanadin kisan sama da mutane dubu goma a bara kamar yadda wata cibiya mai lura da huldodin kasa da kasa a birnin Washington ta bayyana.