Kisan dakarun wanzar da zaman lafiya a Mali
October 3, 2014Talla
Mai magana da yawun dakarun na wanzar da zaman lafiya a Mali din Olivier Salgado ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewar jami'an nasu da aka kashe sun kai tara kuma dukanninsu 'yan Jamhuriyar Nijar ne.
Mr. Salgado ya ce wasu mahara ne a kan babura dauke da manyan makamai suka yi kisan tsakanin garuruwa Menaka da Ansong da ke arewa maso gabashin kasar ta Mali. Wannan dai shi ne hari mafi muni da dakarun suka fuskanta a kasar a baya-bayan nan.