1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin karbe garin Tikrit daga hannun IS

Ahmed SalisuMarch 5, 2015

Ana cigaba da musayar wuta tsakanin 'yan bindiga da dakarun gwamnati a yunkurin da su ke karbe iko da garin nan Tikrit da 'yan IS suka karbe a watan Yunin bara.

https://p.dw.com/p/1EmNZ
Irak Tikrit Offensive gegen IS
Hoto: Reuters/T. Al-Sudani

Shaidun gani da ido dai sun ce mutane da dama sun rasa rayukansu a wannan gumurzu da ake musamman ma lokacin da 'yan bindinga suka afkawa yankunan da fararen hula suka fi yawa.

Dubban mutane ne dai aka yi hasashen za su rasa matsugunansu sakamakon wannan rikici da ake yi. A watan Yunin bara ne dai garin na Tikrit ya fada hannun 'yan kungiyar nan ta IS da ke rajin kafa daular Islama a Irakin da Siriya.