1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin Koriya ta Arewa na kare kanta

Ahmed SalisuApril 9, 2015

Koriya ta Arewa ta ce duk da matsi na tattalin arziki da ta ke fuskanta da kuma karancin abinci, ya zame mata wajibi ta kara karfinta na nukiliya da nufin kare kanta.

https://p.dw.com/p/1F5c0
Nordkorea Soldaten Militärübung
Hoto: dapd

A wani rahoto da aka gabatar gaban majalisar dokokin kasar, Koriya ta Arewan ta ce abinda ta sanya gaba shi ne ta ga ta magance masassarar da tattalin arzikinta ke fuskanta.

Sai da a hannu guda kamfanin dillancin labarai na kasar na KCNA ya rawaito wani kusa a gwamnatin kasar na cewar muhimmancin daidaita al'amura na tattalin arzikin kasar na kan doro guda da kare kasar daga duka wata barazana.

Koriya ta Arewa din dai ta ce za ta kashe akalla kashi 15 cikin 100 na kasafin kudinta na bana kan harkokin da suka danganci tsaro kamar yadda ta yi a shekarar da ta gabata.