1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin neman sulhu a rikicin Siriya

Abdourahamane Hassane
January 25, 2018

Za a sake komawa a kan tebrin tataunawa a yunkurin da ake yi na wanzar da zaman lafiya a Siriya a karkashin jagorancin Majalisar Dinkin Duniya a Vienna.

https://p.dw.com/p/2rTkh
Astana Neue Friedensgespräche zu Syrien-Konflikt
Hoto: Getty Images/AFP/S. Filipov

Wannan tattaunawa dai na zuwa a daidai lokacin da fada ke kara yin muni tsakanin dakarun gwamnatin da na 'yan tawayen a fagen dagga abin da ake gani zai iya yin kafar ungulu ga shawarwarin. Daman dai wata guda da ya wuce an gudanar da irin wannan taro a Geneve ba tare da samun daidaito ba tsakanin bangarorin biyu sakamakon yadda aka gaza yin tattaunwa ta gaba da gaba.