1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kokarin saka wa Koriya ta Arewa takunkumi

August 5, 2017

Majiyoyin diflomasiyya a Amirka sun ce kasar na can ta na matsa wa don samun amincewar kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya a wannan Asabar a kokarinta na ganin an kakaba wa Koriya ta Arewa takunkumi.

https://p.dw.com/p/2hivt
Nordkorea Kim Jong-un
Hoto: Reuters/KCNA

Hakan na zuwa bayan sabbin gwaje-gwajen makamai masu linzamin da ke cin dogon zango da Koriya ta Arewar ta yi. Yanzu dai a shirye kasar ta ke don rarraba daftarin kudurin bukatar hakan ga dukkanin mabobin kwamitin sulhun Majlisar ta Dinkin Duniya wanda tuni kuwa alamu suka nuna samun amincewar kasar China. Da ma dai Amirka da China na shawartawa dangane da tsara daftarin kudurin gabanin wannan matakin da aka kai. Ana bukatar sahalewar kasashe tara daga cikin mambobin kwamitin na sulhu kafin wannan kuduri ya haye.