1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Koriya ta Arewa na son zantawa da Amirka

Ahmed Salisu
February 25, 2018

Wani babban janar na rundunar sojin Koriya ta Arewa ya bayyana wa shugaban Koriya ta Kudu Moon Jae In cewar kasarsa shirye ta ke ta hau teburin tattaunawa da Amirka.

https://p.dw.com/p/2tJ9A
Kombi-Bild  Trump und Kim Jong Un
Hoto: Reuters/K. Lamarque/KCNA

Janar din mai suna Kim Yong Chol ya ambata hakan ne Pyeongchang na kasar Koriya ta Kudu gabannin rufe wasannin Olympics da aka yi a yau (25.02.2018), inda ya ke cewar Pyongyang na da kyakkyawar niyya ta tattauawa da Washington. Amirka da Koriya ta Arewa sun jima su na takun saka sai dai lamarin ya fi kamari tun bayan hawan Donald Trump kan gadon mulki inda ya kasance a sahun gaba na shugannin duniya da ke son ganin an matsawa Arewa din lamba don ta yi watsi da shirinta na kera makaman kare dangi.