1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Irak: Kotu ta bada sammacin Donald Trump

Abdoulaye Mamane Amadou
January 7, 2021

A dai-dai lokacin da hankalin duniya ya karkata kan halin da fagen siyasar Amirka ya shiga, zargin kisan daya daga na hannun daman mai fada a ji a rundunar sojan Iran a Iraki.

https://p.dw.com/p/3ndbi
USA Sturm gegen US-Capitol | Gegenproteste
Hoto: Angela Weiss/AFP/Getty Images

Wata kotu a Iraki ta bada sammacin kama Shugaba Donald Trump, bisa zarginsa da hannu wajen kisan Abou Mehdi al-Mouhandis, daya daga cikin na hannun daman babban kwamandan sojan Iran na juyin juya hali, Janar Qassem Soleimani a shekarar 2020.

Ko a watan Yunin da ya gabata, Iran ta taba aike da wata wasikar neman sammacin Donald Trump ga hukumar 'yan sandan kasa da kasa ta Interpol, sai da har yanzu hakar Iran din ba ta cimma ruwa ba.

Ayar doka mai lamba 406 ta kundin hukunta laifukan Iraki da kotun ta yi amfani da ita wajen zartar da hukuncin sammacin, ta tanadi hukucin rajamu ne kan duk wani wanda yayi kisa da gangan ga wani dan kasar.