1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotu ta ce a bude gidajen talabijin a Kenya

Yusuf Bala Nayaya
February 1, 2018

Kotun ta bada umarni gwamnatin ta kawo karshen rufe manyan gidajen talabijin uku bayan da kafafan yada labaran suka watsa hotunan jagoran adawa a lokacin kwaikwayon rantsuwar kama mulki.

https://p.dw.com/p/2ruy0
Kenia | Proteste gegen den Wahlausgang vor dem Obersten Gerichtshof in Nairobi
Hoto: Getty Images/AFP/T. Karumba

'Yan jarida da 'yan fafutika sun koka da yadda gwamnatin ta rufe kafafan yada labaran daga ranar Talata. Wasu 'yan jaridar sun bayyana cewa sun boye kansu da kwana a ofisoshinsu don gudun kada su fito a kamasu.

Shi dai madugun adawa Raila Odinga ya rantsar da kansa a matsayin shugaban al'umma a kokarin nuna adawa da rantsuwar kama shugabancin Uhuru Kenyatta da aka bayyana da samun nasara a zaben da aka yi a shekarar bara.

Odinga dai ya ce zaben cike yake da kura-kurai a kasar ta Kenya da ke gabashin Afirka.