1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Aung San Suu Kyi za ta kara zaman yari

Abdul-raheem Hassan MAB
January 10, 2022

Wata kotun sojoji a Myanmar ta yanke wa hambararriyar Shugabar kasar Aung San Suu Kyi hukuncin daurin shekaru hudu a gidan yari, bayan samunta da karin laifuka har da mallakar rediyon "walkie-talkie" marar lasisi.

https://p.dw.com/p/45LV5
Aung Suu Kyi plädiert für Myanmar im Friedenspalast
Hoto: Koen van Weel/picture alliance /ANP

An yanke wa tsohuwar shugabar mai shekaru 76 hukuncin daurin shekaru biyu saboda karya dokar shigowa da kaya da kuma mallakar wayoyin tafi da gidanka, sai kuma karin shekara guda na samun sigina.

Gabannin wannan hukuncin, Aung San Suu Kyi na fuskantar tuhuma kan laifuka kusan goma sha biyu wadanda ke da hukuncin dauri na sama da shekaru 100 a gidan yari tun bayan da sojoji suka kifar da gwamnatinta wanda ya haifar da zanga-zangar gama gari, har mutane da dama suka mutu yayin da aka kama wasu masu yawan gaske.