1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

kwana na biyu na yajin aiki a Najeriya

June 21, 2007
https://p.dw.com/p/BuII

A Najeriya an shiga kwana na biyu na yajin aiki na gama gari sakamakon karin farashin albarkatun man fetur a kasar.

Kodayake yajin aikin bai shafi fitar da danyen man fetur din ba zuwa ketare sai dai kuma shugananin kodago sunyi kira ga membobinsu da su tabbatar da cewa an durkusadda tattalin arzikin kasar.

An rufe bankuna da makarantu da gidajen man a sassa da dama na kasar yayinda shugabanin kodago ke ci gaba da tattaunawa da gwamnati.

Yajin aikin ya shafi zirag ziragn jiragen a cikin kasar hakazalika jiragen kasa da kada tilas suke sauka a kasashen makwabta domin shan mai