1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kwango ta ƙulla yarjejeniyar sulhu da M23

December 12, 2013

Ƙungiyar wadda ta daɗe tana fafutuka a yankin gabashin Kwango ta shiga yarjejeniyar da ta tanadi kwance ɗammarar makamai da kuma fiskantar hukunci idan aka same ta da laifukan yaƙi

https://p.dw.com/p/1AYRn
Demokratische Republik Kongo M23 Rebellen Soldaten
Hoto: picture-alliance/dpa

Kwango ta rattaɓa hannu kan wata yarjejeniyar sulhu da Ƙungiyar ta M23. Mai magana da yawun gwamnatin Kwango Lambert Mende ya ce takardu uku aka sanya wa hannu a faɗar shugaban ƙasar Kenya da ke Nairobi, kuma daga cikin abubuwan da suka tanadar har da rusa ƙungiyar M23 a matsayin ƙungiyar da ke fafutuka da makamai, da kuma tuba daga amfani da ƙarfi wajen cimma burinsu.To sai dai Mr Mende ya ce ba kowa ne za a yi wa afuwa ba domin a shirye suke su hukunta duk wanda aka kama da tabka laifukan yaƙi bisa tanadin dokokin ƙasa da ƙasa.

A wani labarin kuma babban kwamandan dakarun wanzar da zaman lafiya a Kwango ya kira wani taron manema labarai domin yin gargaɗi ga ƙungiyar 'yan tawayen FDLR da ke ɓoye a cikin dazukan ƙasar, da su kwance ɗammararsu ko kuma a kwance musu da ƙarfi da yaji. Majalisar Ɗinkin Duniya wadda aka yi ta suka na tsawon shekaru da dama yanzu, bisa gazawarta wajen kawo ƙarshen wannan rikici, ta fara ƙoƙarin farfaɗo da ƙimarta a idon al'ummar ƙasa da ƙasa tun bayan da ta yi nasarar tasa ƙeyar 'yan ƙungiyar M23 waɗanda suka kutsa suka kuma mamaye waɗansu mahimman garuruwa a yankin gabashin Kwango daga farkon wannan shekara.

Mawallafiya: Pinaɗo Abdu Waba
Edita: Abdourahamane Hassane