1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Siyasar Kwankwaso da Ganduje a Kano

Uwais Abubakar Idris LMJ
January 5, 2022

Yunkurin sulhu a tsakanin tsohon gwamnan jihar Kano Dakta Rabiu Musa Kwankwaso da gwamnan jihar mai ci yanzu Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya bar baya da kura.

https://p.dw.com/p/45B5C
DW l Kwankwaso Interview, Nigeria
Tsohon gwamnan Kano Dakta Rabiu Musa KwankwasoHoto: Kwankwasiyya official Foto, Kano Nigeria

Tun dai bayan zaben shekara ta 2015 ne dangantaka ta fara tsami tsakanin Kwankwaso da Ganduje da ya yi masa mataimaki a tsawon mulkin shekaru takwas da ya yi a matsayin gwamnan Kano. Sai dai al'amura sun kara dagulewa a tsakanin mutanen biyu, bayan zaben shekara ta 2019. An yi yunkuri ne da ma haduwa ta gaba da gaba a lokacin da gwamnan Kanon Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya je ya yi wa tsohon gwamnan jihar Dakta Rabiu Musa Kwankwaso ta'aziyya a lokacin rasuwar kanin Kwankwason.

A hira ta musamman da Uwaisu Abubakar Idris  waikilinmu na Abuja ya yi da tsohon gwamnan Kanon Rabiu Musa Kwankwaso ya tabo batutuwa da dama da suka hadar da batun sauya sheka daga jamiyyarsa ta PDP zuwa APC ko zai sake shiga takarar neman shugabancin Najeriyar a 2023. A cewarsa a yanzu dai ba ya tattaunawa da kowa dangane da batun sauyin sheka, kana batun takara lokaci zai nuna. Haka kuma Kwankwason da ke zaman jagoran siyasar Kwankwasiyya a Najeriya, ya tabo batun rashin tsaro da ake fama da shi musamman a yankin Arewaso maso Yammacin kasar.