1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Macky Sall ya lashe zaben Senegal

March 1, 2019

Hukumar zaben kasar Senegal ta sanar da Shugaba Macky Sall a matsayin wanda ya lashe zaben kasar da aka yi a ranar Lahadin da ta gabata.

https://p.dw.com/p/3EI1G
Senegal Präsidentschaftswahlen | Macky Sall
Hoto: picture-alliance/Xinhua News Agency/D. Gueye

Shugaba Macky Sall ya ci zaben ne da kashi 58% na kuri'un da aka kada a cewar hukumar, inda zai sake mulkin kasar na shekaru biyar nan gaba. Abokin takarar Macky Salla, tsohon firamnista Idrissa Seck, ya zo na biyu da kashi 20.5%

Sai dai ba za a sahale wa Shugaba Macky Sall nasarar ba, sai har kotun tsarin mulkin kasar ta tantance tare da tabbatar tsari da kuma abin da hukamar ta sanar.

Jam'iyyun hamayya a Senegal din dai sun yi watsi da sakamakon da hukumar zaben kasar ta bayyana.