1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Magoya bayan Mahaman Ousmane a Nijar sun kafa kwamitin COSMO

Zainab Mohammed AbubakarAugust 4, 2015

Magoya bayan tsohon shugaban jam'iyyar CDS Rahama kana zababben shugaban kasar Nijar na farko sun kafa wannan kwamiti ne domin goyon bayan takararsa a zabe mai zuwa.

https://p.dw.com/p/1G9xB
Mahamane Ousman Ex-Präsident Niger
Hoto: DW/M. Kanta

Kafa wannan komiti na COSMO ya wakana ne bayan da shugabancin jam'iyyarsa ta asali ta CDS Rahama ya kubuce masa a sakamakon kayin da abokin hamayyarsa cikin rikicin neman shugabancin jam'iyyar Alhaji Abdou Labo ya yi masa a gaban kotu.

Bikin kaddamar da wannan kwamiti na goyan bayan Mahaman Usmane ya samu halartar Shugabannin 'yan adawa da dama wadanda a gurin bikin suka sha alwashin tsayawa takara ko ana ha maza ha mata a zaben shugaban kasar mai zuwa duk da tuhume-tuhumen da suke fuskanta gaban kotu.

Tuhume-tuhuman kuma da suke zargin gwamnatin Mahamadu Issoufou da kitsa su domin haramta masu kalubalantarsa a zaben mai zuwa. Zargin da bangaren shugaban kasar ke musantawa.