1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar Dinkin Duniya ta ce a dage zabe a Burundi

Yusuf BalaJune 26, 2015

A ranar Litininin ne dai aka tsara cewa za a yi zaben 'yan majalisar dokoki sannan a yi zaben shugaban kasa a ranar 15 ga watan Yuli.

https://p.dw.com/p/1Fnru
Ban Ki-moon
Hoto: picture-alliance/dpa/I. Kovalenko

Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya a ranar Juma'an nan ya bukaci mahukunta a kasar Burundi su gaggauta yin duba ga shirin dage zaben kasar duba da halin da demokradiyar kasar ta samu kanta ga rashin tsaro.

Sakatare Ban Ki-moon ya mara baya ga kiraye-kirayen kasashen yamma da na Afirka wadanda su ka bukaci a dage zaben bayan da kasar ta shiga rudani bayan zanga-zangar adawa da shirin neman tazarcen shugaba Nkurinziza a karo na uku.

A ranar Litininin ne dai aka tsara cewa za a yi zaben 'yan majalisar dokoki sannan a yi zaben shugaban kasa a ranar 15 ga watan Yuli. Zaben da 'yan adawa su ka ce za su kaurace masa.