1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar dokokin Girka ta amince da shirin tsimin gwamnati

Salissou BoukariJuly 11, 2015

Da gagarumin rinjaye wakilan majalisar dokokin ta Girka sun amince da sabbin matakan da Firaministan kasar Tsipras ya gabatar wa masu ba wa kasar bashi don ceto tattatlin arzikinta.

https://p.dw.com/p/1FxD6
Griechenland / Parlament / Sparprogramm
Hoto: Reuters

Majalisar dokokin kasar Girka ta bada amannarta kan tsarin shawarwarin da gwamnatin kasar ta fitar wadanda za su kasance madogara a ci gaba da tattaunawar da kasar za ta yi da masu biyarta bashi da suka hada da Tarayyar Turai, da babban bankin Turai da kuma asusun bada lamuni na duniya wato IMF.

Sai dai duk da haka Firaministan na Girka Alexis Tsipras, ya fuskanci bijirewar wasu daga cikin 'yan majalisun na jam'iyyarsa ta Syriza akalla guda goma, inda biyu daga cikinsu suka kada kuri'ar kin amincewa, yayin da takwas kuma suka ce baruwansu.

Daga cikin takwas din da suka ce ba ruwansu, akwai ministoci biyu da kuma shugaban majalisar kanshi Zoe Konstantopoulou, da ke a matsayin na uku a kasar ta Girka. Ga baki daya dai 'yan majalisa 251 ne daga cikin 300 suka kada kuri'un amincewa da wannan tsari.

Tuni dai masu lura da al'amura ke ganin cewa, nokewar da wasu ministocin gwamnatin suka yi na iya janyo garambawul a majalisar ministocin kasar ta Girka.