1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Malala Yousafzai ta isa a kasarta ta Pakistan

Salissou Boukari
March 29, 2018

Malala Yousafzai, ta isa a birnin Islamabad na kasar Pakistan a karon farko tun bayan da 'yan kungiyar Taliban suka kai ma ta hari a shekara ta 2012.

https://p.dw.com/p/2vAIA
Malala Yousafzai
Malala Yousafzai ta sauka a birnin Islamabad na PakistanHoto: Reuters/E. Garrido

Wannan dai shi ne karo na farko da Malala ta isa a wannan kasa tata ta haihuwa, tun bayan da 'yan kungiyar Taliban suka harbeta da bindiga bisa kai a shekara ta 2012. Inda aka fice da ita ya zuwa birnin London na Birtaniya aka yi ma ta magani, sannan ta ci gaba da karatunta. Da yake magana kan wannan ziyara ta Malala a kasar ta Pakistan, mai magana da yawun ofishin ministan harkokin wajen kasar Muhammad Faisal, ya ce suna masu yin maraba da zuwan Malala a gida Pakistan, inda ya kara da cewaR matashiyar mai shekaru 20 da haihuwa da ke fafutikar kare incin ilimin diya mata, za ta gana da mutane da dama a kasar, sai da kuma ba a sanar da wuraran da za ta bi ba ta sabili da dalillai na tsaro.