1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gobara ta tashi a cocin Kobdawa a Masar

Abdul-raheem Hassan
August 14, 2022

Wasu majiyoyi sun ce wutar lantarki ce sanadin tashin gobarar a lokacin da mutane akalla 5,000 ke addu'a a majami'ar a ranar Lahadi. Gwamnati ta kaddamar da bincike don gano tushen gobarar.

https://p.dw.com/p/4FVyF
Masar, Giza | Gobara, Coci
Hoto: Mohamed Abd El Ghany/REUTERS

Rahotanni daga Masar na cewa fiye da mutane 40 sun mutu wasu 55 sun jikkata, sakamakon tashin gobara a wata majami'ar 'yan Kibdawa da ke birnin Giza a wajen Alkahira.

Kibdawa su ne mafi girma a cikin al'ummar Kirista a yankin Gabas ta Tsakiya, a kusan mutane miliyan 10 daga cikin adadin 'yan Masar miliyan 103.

‘Yan tsirarun dai sun sha fama da hare-hare tare da kokawa da nuna wariya a kasar Musulmi mafi rinjaye a arewacin Afirka, wadda ta fi kowacce yawan al'umma a kasashen Larabawa.