1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masar na zaben raba gardama

April 20, 2019

Yayin da wutar juyin juya hali ke ci a wasu kasashen Afirka, Masar na zaben tabbatar da Shugaba al-Sisi kan karagar mulki na wasu shekaru nan gaba.

https://p.dw.com/p/3H7zI
Ägypten Präsident Abdel Fattah al Sisi
Hoto: picture-alliance/dpa/Sputnik/V. Belousov

A kasar Masar, ana ci gaba da zaben raba gardama bayan gyaran fuska da majalisa ta yi wa kundin mulkin kasar, da ka iya bai wa shugaban kasa damar zarcewa zuwa shekara ta 2030.

Tashar talabijin ta kasar ta nuno Shugaba al-Sisi lokacin da yake kada kuri'arsa da misalain karfe tara na safiya, da ma na wasu misrawan asassa daban-daban.

Sama da mutum miliya 61 aka yi wa rajistar zabe a Masar din wanda zai dau kwanaki uku.

Haka nan ma sauye-sauyen za su bai wa shugaban kasar damar nada manya a bangaren shari'a da kuma taka gagarumar rawa a kan al'amuran sojin Masar.

Zaben na zuwa ne yayin da wutar juyin juya hali ke ci a wasu yankunan larabawa da ke nahiyar Afirka, da masu da'awar jaddada dimukuradiyya ke turje wa masu mulki na mahadi ka ture.