1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

wata kotun ɗaukaka ƙara a masar ta soke wani hukuncin kotu

Abdourahamane HassaneJune 6, 2015

Wata kotun ɗaukaka kara ta soke wani hukuncin kotun wanda ya saka Hamas a cikin ƙungiyoyin 'yan ta'adda

https://p.dw.com/p/1Fcgh
Gaza Ägypten Proteste Symbolbild
Hoto: MOHAMMED ABED/AFP/Getty Images

Wani babban jami'n kula da harkokin shari'a a ƙasar ta Masar ya shaida wa manema labarai cewar an jingine hukunci ne domin kotun da ta zartar da shi ba ta da hurumin yin haka.

A ƙarshen watan Janairun da ya gabata ne kotun ta yanke hukunci a kan Ƙungiyar ta Hamas mai iko da Yankin Zirin Gaza na Falasɗinu kana kuma aka haramta wa ƙungiyar taɓa kuɗaɗenta na ajiya a cikin bankuna.Gwamnatin ta Masar na zargi Hamas da taimaka wa reshen Ƙungiyar IS a yankin Sinai wacce ke kai hare-hare a kan jami'an tsaro.Dangantaka tsakanin Hamas da Masar ta yi tsami tun bayan faɗuwar gwamnatin Mohammed Morsi a shekarun 2013.