1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masar ta soki Isra'ila kan dokar kasar Yahudawa

Yusuf Bala Nayaya
July 21, 2018

Kasar Masar ta bayyana a wannan Asabar cewa matakin da Isra'ila ta dauka na bayyana Isra'ila a matsayin kasar Yahudawa zalla baban kuskure ne kuma ta guji abin da zai biyo baya.

https://p.dw.com/p/31rUO
Ägypten Präsident Abdel Fattah al-Sisi
Hoto: picture-alliance/Zumapress/President Office

Kasar Masar dai ta kasance kasar Larabawa ta farko da ta kulla yarjejeniyar zaman lafiya da Isra'ila a shekarar 1979 matakin da ya kawo karshen shekaru da dama na zaman doya da manja tsakanin kasashen. A cewar ma'aikatar harkokin wajen Masar bayyana kasar Isra'ila a matsayin kasar Yahudawa zalla zai haifar da wariya da yin zagon kasa ga shirin zaman lafiya da ake son kullawa a kasar.