1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Maslaha game da yakin basasar Siriya

November 11, 2013

A yanzu 'yan adawar Siriya sun bayyana kudirin halartar taron sulhu na Geneva.

https://p.dw.com/p/1AF6S
epa03942203 (L-R) Member National Coalition Of Syria Suheir Atassi, Head of the Syrian National Coalition, Ahmad al-Jarba, Secretary General National Coalition of Syria Badr Jamous, Member National Coalition Of Syria Salim Muslit, Leaders of the exiled Syrian National Council (SNC), Muhammet Faruq Tayfur during a Syrian opposition groups meeting in Istanbul, Turkey, 09 November 2013. A plan for Syrian peace talks failed to materialize on 06 November 2013 after Russian, US and UN officials did not agree on when to hold them or which countries to invite, international envoy Lakhdar Brahimi said. EPA/SEDAT SUNA
Hoto: picture-alliance/dpa

'Yan adawar kasar Siriya da ke samun goyon bayan kasashen yammacin duniya sun sanar da cewar, za su halarci taron kasa da kasa domin samar da mafita ga rikicin kasarsu, wanda birnin Geneva zai kaibi bakunci. Wannan labarin na kunshe ne cikin wata sanarwar da hadaddiyar kungiyar 'yan adawar kasar ta Siriya ta fitar da safiyar wannan Litinin (11. 11. 13). Sai dai kuma 'yan adawar sun bada sharadin cewar, tilas ne a samar da wata gwamnatin wucin gadin da za ta mayar da Siriya bisa turbar dimokradiyya a matsayin hanyar kawo karshen yakin basasar kasar na tsaawon kimanin shekaru biyu da rabi kenan.

Hakanan sun gindaya sharadin bayar da dama ga hukumomin bayar da agaji kai wa ga yankunan da ake yi wa kawanya, da kuma sakin fursunonin siyasa, game da cewar, tilas ne duk wani babban taron da ya shafi siyasa ya kasance yana da manufar tsara hanyar komawa kan tafarkin siyasa a kasar. Sai dai kuma akwai wani bangare na 'yan tawayen da yayi watsi da halartar taron na Geneva, muddin dai ba zai kai ga cire shugaba Assad daga mulki ba, kana akwai ma wasu 'yan tawayen da suka ce za su dauki duk wanda ya halarci taron a matsayin wanda ya ci amanar kasar.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Umaru Aliyu