1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mata na daɗa samun muƙamai a kotunan Najeriya

Usman ShehuNovember 23, 2012

A Tarayyar Najeriya ana samun ƙarin mata a fannin shari'ar ƙasar, inda yanzu aka naɗa Zainab Adamu Bulkachuwa a matsayin shugabar kotun ɗaukaka ƙara ta Tarayya

https://p.dw.com/p/16ozU
Themis relief without blindfolded
Hoto: Fotolia/toluk

A ci gaba da kokarin sa na neman mafita a cikin rikicin da ya yi aure ya kuma kama hanyar tarewa a cikin sashen shari'ar Tarayyar Najeriya, an rantsar da shugaba ta uku cikin tsawon watanni 15 ga kotun daukaka karar kasar dake zanman ta biyu mafi girma a tsarin shari'ar kasar.

Hankali dai ya tashi a kusan daukacin kasar ta Najeriya a lokacin da alkali na biyu mafi girman iko ya kalli na farko a ido ya zarge shi da kokarin son rai a wani ƙarin girman da ya samu ya zuwa kotun koli.

Supreme Court Abuja.jpg
Hoton ginin kotun ƙolin NajeriyaHoto: DW

Mai shari'a Isa Ayo Salami dai yace akai kasuwa game da batun zuwansa kotun kolin da  a wancan lokaci babban alkalin kasar mai sharia Alosius Katsina Alu ya bukace shi da yi. Abun kuma da ya kai ga bude sabon babi ya kuma kai ga fito fili tsohon karatun cin hancin da ake ta'allakawa da sashen shari'ar kasar ta Najeriya.

An dai share tsawon watttani har 15 ana kai kawo, an kuma kai ga nadin akalla shugabanni biyu ga kotun daukaka karar kasar dake zaman ta biyu mafi girma kuma ke cikin tsakiyar rikicin.

Ta baya baya dai na zaman mai sharia Zainab Adamu Bulkachuwa da aka kai ga rantsarwa a yau da kuma ke zaman shugaba ta uku cikin tsawon lokaci.

Mace ta farko da zata ja ragamar kotun dai mai sharia Bulkachuwa na da jan aikin sake dawo da kima da martabar sashen shari'a, da yanzu haka ke cikin rudani

Babban kalubale a gaban sabuwar shugabar dai a cewar Barrister Waziri Mamman dake zaman wani lauya mai zaman kansa dai, shine tunkarar matsalar cin hancin a matakai daban daban na kotun.

epa03046192 (FILE) A file photograph Nigerian president Goodluck Jonathan (2-L) standing on the back of a vehicle as he is driven after he was sworn in as president during a ceremony in Abuja, Nigeria 29 May 2011. Media reports state on 31 December 2011 that President Goodluck Jonathan has declared a state of emergency in areas affected by attacks from the Islamist group Boko Haram. Borders will be temporarily closed in the north-eastern states of Yobe and Borno, and central state of Plateau. EPA/STR *** Local Caption *** 00000402757844
Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan a binkin rantsuwar kama aikiHoto: picture-alliance/dpa

To sai dai koma ta ina take shirin farawa dai ana hasashen da kamar wuya ga sabuwar alkaliyar ta kai ga iya kawo sauyin da ake fatan gani a cikin kotun da ke taka muhimiyyar rawa ga batun shari'u na siyasa da kuma ake zargi da kasancewa babbar matattarar cin hancin na shari'un da suka shafi siyasa.

An dai ambato sunan ita kanta sabuwar alkaliyar a cikin wasu daga cikin shari'un da masharhanta ke ganin da sauran gyara a cikinsu, abun kuma da a cewar Mallam Garba Umar dake zaman masanin harkokin zamantakewar kasar ya sa da wuyar gaske a kai tudun mun tsirar shari'ar da yan kasar ke fatan gani a yanzu.

Akwai dai masu kallon sabon sauyin a matsayin kama hanyar kawo karshen fatan tsohon shugaban kotun mai shari'a Isa Ayo Salami na sake ɗana kujerar shugaban kotun, duk da cewar dai har ya zuwa yanzu ba ta kai ga karewa a cikin shari'ar da ake tafkawa ba.

Mawallafi: Ubale Musa

Edita: Usman Shehu Usman