1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matakan soji a matsayin zabin magance rikicin Siriya

Kamaluddeen SaniJanuary 23, 2016

Amirka ta ce a shirye take domin tinkarar magance matsalar kungiyar IS idan duk kokarin kawo karshen rikicin cikin lumana ya gagara.

https://p.dw.com/p/1Hiy5
Joe Biden und Ahmet Davutoglu in Istanbul
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Suna

Mataimakin shugaban kasar Amirka Joe Biden ya jaddada cewar kasashen Amirka da Turkiyya a shirye suke domin daukar matakin soji a matsayin hanyar magance ayyukan ta'addanci gami da yakar kungiyar IS a Siriya a duk lokacin da gwamnatin kasar da 'yan tawaye suka gaza wajen samun maslahar siyasar kasar.

Joe Biden ya furta kalaman ne a wani taron manema labarai da suka gudanar tare da Firaministan Turkiyya Ahmet Davutoglu a birnin Istanbul na kasar Turkiyya a dai-dai lokacin da ake shirye-shiryen fara wata tattaunawar zaman lafiyar Siriyan a birnin Geneva a ranar Litinin mai zuwa.

Ya ce: "Ko tantama babu a shirye muke a kan wannan matakin, John Kerry yana ganawa da mahukuntan Saudiyya a dai-dai lokacin da muke wannan maganar, kana za mu gana a birnin Davos a inda Firaminista da ni muka gana da takwarorinmu."

Kazalika Biden ya kara da cewar shi da Firaminista Ahmed Davutoglu sun tattauna a kan yadda za su tallafa wa 'yan tawayen da ke fafutukar ganin sun kawar da shugaba Bashar Al-Assad daga mulki.