1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matsalar fyade a jamhuriyyar Dimokradiyyar Kongo

March 26, 2013

Birtaniya ta yi alkawarin tallafawa wadanda matsalar fyade ta shafa a Kongo

https://p.dw.com/p/184es
Congolese women cheer during the global rally "One Billion Rising", which is part of the V-Day event calling for an end to gender-based violence, in Bukavu February 14, 2013. V-Day is a global activist movement to end violence against women and girls. REUTERS/Jana Asenbrennerova (DEMOCRATIC REPUBLIC OF THE CONGO - Tags: SOCIETY CIVIL UNREST)
Hoto: Reuters

Sakataren kula da harkokin wajen Birtaniya William Hague ya bayyana cewar kasarsa sa za ta samar da kudaden da za'a yi anfani da shi wajen tattaro bayanan da suka shafi wadanda 'yan tawaye suka yi musu fyade a lokacin tashe tashen hankulan da jamhuriyyar Dimokradiyyar Kongo ta fuskanta. Sakataren harkokin wajen na Birtaniya, wanda ya kai ziyarar aiki zuwa Kongo, tare da rakiyar wata fitacciyar 'yar wasan Film nan a kasar Amirka Angelina Jolie, domin nuna damuwa game da matsalar yin anfani da fyade a matsayin makami a lokacin yaki, ba su sami zuwa asibitin Bukavu da ke yankin gabashin Kongon ba, saboda rashin kyawun yanayi. A dai asibitin ne malaman jiyya ke kula da wadanda matsalar fyaden ta addaba. Ofishin kula da harkokin ketare na Birtaniya ya ce dama an shirya sakataren, zai gana tare da likitocin kungiyar kare hakkin jama'a, wadanda ke tallafawa marasa lafiyar. Hague ya bayyana kudirin bayar da gudummowar kudin daya kai Euro dubu 205 domin tattara bayanan.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Mohammad Nasir Awal