1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matsalar yinwa a Tchad

March 30, 2007
https://p.dw.com/p/BuOf

Hukumar samar da abinci ta Majalisar Ɗinkin Dunia, ta bayyana matsanacin halin ƙarancin abinci, da al´ummomin ƙasar Tchad, su kimanin dubu 130 ke fuskanta, a sanadiyar halin gudun hijira ,da su ka tsinci kan su a ciki.

Kakakin hukumar, Christiane Berthiaume ta ce dukkan wannan mutane, sun ƙaura daga gidajen su, a dalilin tashe-tashen hankulla a yankin Darfur na ƙasar Sudan.

Domin kawo tallafi ga wannan jama´a, hukumar na bukatar a ƙalla dalla milion 7 da rabi, ta fannin abinci barguna da magungunna.

Bayan mutanen Ƙasar Tchadin, hukumar na kai agaji ga ƙarin yan gudun hijira Sudan, kussan dubu 250, da ke tsugune a iyakar Tchadi.