1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabon hari ya kashe sojojin Burkina Faso

Abdul-raheem Hassan
April 22, 2021

Babu kungiyar da dau alhakin harin da ya kashe sojojin a lokacin da suke aikin sintiri, sai dai jami'an tsaro sun sha alwashin daukar fansa.

https://p.dw.com/p/3sM7x
Burkina Faso Anschlag ARCHIV
Hoto: picture-alliance/dpa/A. Yempapou

Rahotanni daga Ougadugu babban binrin kasar Burkina Faso na cewa akalla sojoji hudu sun mutu wasu 12 sun jikkata a wani harin kwantan bauna da mahara dauke da manyan makamai suka kaddamar.

Kasar Burkina Faso na cikin kasashen yankin Sahel da ke fuskantar barazanar mayakan jihadi tun bayan da suka kaddamar da kai hare-hare a kasar Mali a shekarar 2015.