1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

IS ta kashe sojojin Mali 35

Abdul-raheem Hassan
November 2, 2019

Wani sako da rundunar ta wallafa a shafinta na yanar gizo, na cewa 'yan ta'addan sun yi wa dakarunta kwanton bauna a sansaninsu da ke arewacin kasar ta kan iyaka da Nijar.

https://p.dw.com/p/3SMVs
Mali Symbolbild Armee | Operation Barkane - Stützpunkt
Hoto: Getty Images/AFP/A. Jocard

Rahotanni daga Bamako babban birnin kasar Mali na cewa adadin sojojin da suka mutu a harin ta'addancin ya kai 35. Wannan sabon hari na zuwa ne kasa da wata guda bayan wani hari da ya halaka sojojin Malin har 38 a wasu sansanoni biyu, arewaci da tsakiyar Mali na cikin tsaka mai wuya na hare-haren ta'addanci tun bullar 'yan aware a shekarar 2012.

Duk da cewa akwai sojojin hadin gwiwa da ke yakar ayyukan ta'addanci a kasar Mali, amma har yanzu 'yan bindiga na barazana ga rayuwar fararen hula da jami'an tsaro.