1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD: Mutane na fama da matsala a Yemen

May 10, 2017

Majalisar Dinkin Duniya ta ce bisa ga dukkan alamu mutum dubu 500 na iya shiga mawuyacin hali a yankin Arewa maso yammacin kasar Yemen muddin aka gaza daukar matakai cikin hanzari.

https://p.dw.com/p/2clPZ
Jemen Kampfhubschrauber tötet offenbar Dutzende Flüchtlinge
Hoto: Reuters/A. Zeyad

Kakakin hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD a lardin Taez na Yemen Shabiya Mantoo, ya ce daruruwan mutane ne suka rasa muhallinsu kuma ke fama da karancin abinci, duk da cewa rikici bai kazanta ba a kasar, kuma galibinsu a yankin Hudeida ne.

A cewar jami'in a halin da ake ciki akwai mata da kananan yara masu yawa da ke barar abin da za su ci a manyan tituna, sakamakon yawan jama'ar da ta yiwo hijira shekaru biyun da suka gabata.

Akalla rayuka mutam dubu 7 da 700 ne suka salwanta yayin da wasu miliyoyi suka rasa muhalli, sakamakon rikici a Yemen a shekara ta 2015.