1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD ta bukaci bincike kan kisan fararan hula a Bama

October 25, 2016

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci gwamnatin kasar Bama ko Myanmar da ta gudanar da bincike kan al'amarin kisan farararn hula da sojoji suka yi da ma kone wasu kauyika a Yammacin kasar a makonnin baya bayan nan

https://p.dw.com/p/2RgNy
Sittwe Kämpfe zwischen Muslimen und Buddhisten
Hoto: Reuters

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci gwamnatin kasar Bama ko Myanmar da ta gudanar da bincike kan al'amarin kisan farararn hula da sojoji suka yi da ma kone wasu kauyika a Yammacin kasar a makonnin baya bayan nan. Lamarin da ya tilasta wa dubunnan mutane tserewa daga garuruwansu domin tsira da rayukansu.

Majalisar Dinkin Duniyar ta bayyana wannan matsayi nata ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a Yammacin jiya Litinin inda ta ce gwamnatin kasar ta Bama ba ta da hujjar kisan mutane a bisa zargi kawai na aikata wani babban laifi. 

A farkon wata Oktoban nan ne dai bayan wani hari da aka kai kan wani ofishin 'yan sanda, gwamnatin kasar ta Bama ta tura sojoji a yankin inda suka yi ta kisan musulmai 'yan kabilar Rohingyas a bisa zargin cewa daruruwan daga cikinsu da suka samu horo daga Kungiyar Taliban ke da alhakin kai wannan hari.