1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD ta ce soji su kaucewa shiga siyasa Iraki

August 11, 2014

Bayan da shugaban kasar Iraki ya bayyana Haidar al-Abadi ya maye gurbin al-Maliki a matsayin sabon firaminista, magoya bayan Maliki sun bayyana adawarsu.

https://p.dw.com/p/1Csee
Irak Haider Al Abadi nominiert als Premierminister Archiv 15.07.2014
Hoto: picture-alliance/dpa

Majalisar Dinkin Duniya ta gargadi Jamian tsaro a Iraki da kada su tsoma bakinsu a harkokin siyasar kasar bayan da shugaban kasar ya bayyana sunan wanda zai maye gurbin al-Maliki a matsayin sabon firaminista.

Jakadan MDD a Iraki Nickolay Mladenov shi ya bayyana haka: "Duk wani yunkuri da zai sanya a ga hannun soji a harkokin siyasar kasar abin kyamane".

Bayan da shugaba Masum ya amince da zabin kawancen jamiyyar bangaren 'yan shia da suka amince da Haidar al-Abadi,magoya bayan Maliki sun tattaru a tsakiyar birnin Baghadaza dan nuna adawarsu.

Tun ma dai a yammacin ranar Lahadi ne aka samar da jamian tsaro na farin kaya da 'yan sanda da soji a wasu fitattun wurare a birnin na Baghadaza kafin daga bisani Nuru al-Maliki ya bayyana a kafar talabijin cewa zai gurfanar da shugaban kasar a gaban kuliya idan yaki bayyana shi a matsayin firaminista.

Mawallafi: Yusuf Bala
Edita: Pinado Abdu Waba