1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

MDD: Mutane miliyan 29 na neman agaji a kasashen Sahel

April 28, 2021

MDD ta sanar da cewa kimanin mutum miliyan 29 ne ke bukatar agaji a kasashen Sahel, tana mai nuna yadda matsalar tsaro da yunwa ke kara karuwa a tsakanin mutanen kasashe shida na yankin. 

https://p.dw.com/p/3sfMH
Nahrungsmittel Herstellung Gesundheit
Hoto: picture-alliance/dpa

Daraktan Yanki na Shirin Samar da Abinci na MDD Chris Nikoi a cikin sanarwar da ya fitar a ranar Talata ya ce a kasashen Burkina Faso da arewacin Kamaru da Chadi da Mali da Nijar da kuma arewa maso gabashin Najeriya akwai karin sabbin mutane miliyan biyar da ke bukatar agaji idan an kwantata da shekarar da ta gabata. 

MDD ta ce yawaitar tashin farashin kayan abinci da rashin tsaro ke haddasawa a kasashen Sahel din na haifar da matsananciyar yunwa da karancin abinci a tsakanin al'umma, tana mai gargadin cewa mutane miliyan 29 da ke bukatar agajin ba wai a rubuce kawai suke ba, suna nan a zahiri kuma suna rayuwa cikin kunci.