1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Michel Djotodia ne sabon shugaban Seleka

July 12, 2014

'Yan tawayen Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya sun aminceda tsohon shugaban kasa Michel Djotidia a matsayin jagoran kungiyarsu da ta haddasa rikicin addini a kasar.

https://p.dw.com/p/1Cbqx
Hoto: Getty Images/Afp/Eric Feferberg

Kungiyar 'yan tawayen Seleka na Jamhuriyar Afirka ta TSakiya ta sake bayyana tsohon shugaban kasar Michel Djotodia da ya dare kan karagar mulki bayan da ya jagoranci kungiyar ta samu nasarar kifar da gwamnatin Francois Bozize a matsayin shugabanta.

Rahotanni sun bayyana cewa kungiyar ta ma sake nada wasu daga cikin tsoffin shugabanninta a matsayin shugwabanninta na yanzu a yayin babban taron da ta gudanar. Rikicin addini dai ya barke a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiyar tun bayan da Djotodia ya dare kan karagar mulki wanda hakan ne kuma ya tilasta masa sauka daga karagar mulkin a watan Janairun da ya gabata.

A yanzu haka dai dubun dubatar 'yan Jamhuriyar Afirka dta Tsakiyarne aka tilastawa kauracewa gidajensu yayin da wasu daruruwa suka hallaka sakamakon kisan da 'yan kungiyar tawayen Anti-Balaka ta Kiristocin kasar kewa Musulmi.

Mawallafiya: Lateefa Mustapha Ja'afar

Edita: Mouhamadou Awal Balarabe