1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ministan raya kasa na Jamus na ci gaba da ziyara a Najeriya

June 12, 2014

Gerd Müller ya ce za a karfafa hadin kai tsakanin Jamus da Najeriya a fannonin ilimi musamman ga 'ya'ya mata tare kuma da kare hakkin mata.

https://p.dw.com/p/1CHLo
Bundesentwicklungsminister Gerd Müller in Nigeria 11.6.2014
Hoto: picture-alliance/dpa

Ministan kula da ayyukan raya kasa na tarayyar Jamus Gerd Müller yana Abuja babban birinin tarayyar Najeriya a ci gaba da ziyarar aikin da yake kai wa wannan kasa. A taron manema labaran da yayi dazun nan a Abuja ministan ya zayyana jerin ayyukan hadin kai guda hudu da Jamus da Najeriya za su fi mayar da hankali kansu, inda ya ce: "Za mu karfafa hadin guiwa a bangarorin ilimi musamman ga yara mata da koyon sana'o'i da binciken kimiyya a fannin samar da isasshen abinci a cikin kasa, za mu kuma kara ba da tallafi a bangaren kare hakkin mata da kuma 'yan mata."

Ziyarar minister Müller ta zo ne a daidai lokacin da hare-haren kungiyar Boko Haram suka karu a Najeriya. An dai shirya tattaunawa tsakaninshi da shugaba Goodluck Jonathan da shugaban hukumar kungiyar ECOWAS Kadre Desire Ouadraogo da kuma masu fafatukar neman ceto 'yan matan Chibok na "Bring back our girls". A ranar Laraba ministan ya kai ziyara jihar Ogun da ke kudu maso yammacin Najeriya.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Umaru Aliyu