1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ministocin kudin kasashen Turai za su gana kan kasar Girka

Suleiman BabayoJune 18, 2015

Rashin bai wa kasar Girka kudaden da take bukata zai iya jefa kasar cikin rudadin tattalin arziki tare da fice daga kasashe masu amfani da kudin Euro

https://p.dw.com/p/1Fisn
Griechenland Proteste in Athen
Hoto: Reuters/Y. Behrakis

A wannan Alhamis ministocin kudin kasashen Turai ke ganawa a Luxembourg inda za su tattauna yuwuwar amincewa da bai wa kasar Girka kudade, domin ta kauce daga fadawa cikin matsalolin tattalin arziki.Wani rahoto daga babban bankin kasar ta Girka ya nuna cewa rashin samun kudaden zai jefa kasar cikin kasadar ficewa daga kasashen Turai masu amfani da kudin bai daya na Euro.

A wani lokaci da safiyar wannan Alhamis ake sa ran shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel za ta fitar da sanarwa kan halin ceton tattalin arzikin kasar ta Girka.