1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Musulmai sun fara azumin watan Ramadan na bana

Suleiman BabayoJune 6, 2016

Musulmai a galibin kasashen duniya sun tashi da azumi a wannan Litinin sakamakon ganin jaririn watan Ramadan.

https://p.dw.com/p/1J10J
Symbolbild Ramadan
Hoto: picture-alliance/dpa/N. Mounzer

Galibin Musulmai a kasashen duniya sun fara azumin watan Ramadan da ya daga cikin muhimman rukunan addinin. A ranar Lahadi mahukunta a Saudiyya sun bayyana cewa sakamakon ganin jaririn watan Musulmai a kasar sun tashi da azumin a wannan Litinin.

Kuma akwai kasashe da dama na Musulmai da suka bayyana haka, ciki har da Najeriya. A karshen watan za a yi bukukuwa na Sallah.