Mutane 40 sun hallaka a hare-haren Iraki
September 3, 2013Talla
Jami'an tsaro dai sun ce motoci takwas ne makare da bama-bamai suka tashi a yankuna daban-daban na Bagadazan, kuma wannan ibtila'i ya faru ne kusan lokaci daya, daidai sanda jama'a ke zazzaune a wuraren shan shayi kamar da aka saba da yammaci a birnin.
Kawo yanzu dai babu wata kungiya da ta dauki alhakin kai hare-haren da ma dai dalilin yin hakan sai dai mabiyya tafarkin Sunnah a birnin sun ce suna zargin wadanda ke da alaka da kungiyar nan ta Al-Qaida da kai harin.
A dan tsakannin dai Iraki na shan fama da hare-hare makamantan wannan, inda mahukuntan kasar suka ce suna aiki ba dare ba rana wajen kawo karshensa.
Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Umaru Aliyu