1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane biyu sun mutu a zanga-zangar kenya

Abdul-raheem Hassan/ MABJune 6, 2016

'Yan adawa na nema a rusa hukumar zaben kasar Kenya. Wannan ya haddasa zanga-zangar da ta halaka rayukan mutane biyu a yammancin kasar.

https://p.dw.com/p/1J1NG
Kenia Ausschreitungen und Gewalt in Nairobi
Hoto: Reuters/G. Tomasevic

Mutane biyu sun mutu yayin da wasu shida suka jikata a wata zanga-zanga da ya gudana a birnin Kismu da ke yammacin kasar kenya. 'Yan adawa ne suka shirya wannan sabuwar zanga-zanga don neman gwamnati ta rusa hukumar zaben kasar.

Shaidun gani da ido sun ce jami'an 'yan sanda sun yi harbe-harben kan mai uwa da wabi. Sai dai Sufeto Janar na 'yan sandan kenya Joseph Boinet ya ce sun tarwatsa zanga-zangar saboda haramtacciya ce.

Ya ce "Kotu ta gargadi duk kungiyoyin da ke da niyar shirya-shirya zanga-zanga da su fara neman izini daga hukumomi kasar tukuna. "