1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane da dama sun rasu a hare-haren Iraki

Ahmed SalisuOctober 13, 2014

Wasu jerin hare-haren na bam da aka kai har sau uku sun yi sanadiyyar rasuwar mutane 25 a wasu yankunan Bagadaza wanda galibin mazaunansu mabiya tafarkin Shi'a ne.

https://p.dw.com/p/1DV8I
Irak Anschlag in Kirkuk
Hoto: MARWAN IBRAHIM/AFP/Getty Images

Jami'an 'yan sandan suka ce biyu daga cikin hare-haren na kunar bakin wake ne kuma an kai su ne a birin Sadr yayin da aka kai cikon na ukun birnin Kadhimiyah lokacin da ake gudanar da shagulgulan bikin sallah da suka yi wa lakabi da Eid al-Ghadir.

Ma'aikatar cikin gidan Irakin da ta tabbatar da wannan labarin ta ce baya ga wanda suka rasu, da dama sun samu raunuka wasunsu ma munana kuma hare-haren sun wakana ne lokacin da jama'a ke tsaka da gudanar da harkokinsu.

Ya zuwa yanzu dai ba a kai ga tantance ko wacce kungiya ce ta kai wannan hare-hare ba ko ma dalilin yin hakan.