1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane shida sun mutu a cikin harin Bam a Somaliya

Gazali Abdou TasawaJuly 26, 2015

An kai harin ne a wannan Lahadi da wata mota shaƙe da abubuwa masu fashewa a Hotel Jazeera ta birnin Mogadiscio.

https://p.dw.com/p/1G4yQ
Somalia Shebab Miliz Angriff auf Hotel in Mogadischu
Hoto: AP

A ƙasar Somaliya aƙalla mutane shida akasarinsu jami'an tsaro sun halaka a sakamakon wani hari da aka kai a yammacin Lahadin nan a babban birnin ƙasar Mogadiscio. Hukumomin 'yan sanda ta birnin na Mogadiscio sun shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewar an kai harin ne da wata mota shaƙe da ababe masu fashewa a Hotel Jazeera wacce ga al'ada mambobin gwamnatin ƙasar ta Somaliya dama jami'an diplomasiyyar ƙasashen ketare da ke a ƙasar dama kuma 'yan yawan buɗe ido suke zama cikinta

Tuni dai Ƙungiyar Alshebab ta ɗauki alhakin kai wannan hari inda kakakinta Cheikh Abdiasis Abu Musab ya ce sun kai harin ne a kan sojojin rundunar tsaro ta Afirka ta Amisom dama mambobin gwamnatin ƙasar ta Somaliya a matsayin martani ga jerin hare-haren da suke ta ƙaddamarwa a kan mayakan Ƙungiyar ta Alshebab.