1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutum na bakwai ya mutu da cutar Ebola a Najeriya

September 3, 2014

Hukumomin kiwon lafiya sun ce mutumin ya mutu a kudancin ƙasar

https://p.dw.com/p/1D66G
Sierra Leon Ebola Beerdigung Opfer 14.08.2014
Hoto: AFP/Getty Images

Ministan kiwon lafiya na Najeriya ya sanar da cewar mutun na bakwai wanda ke ɗauke da cutar Ebola ya mutu a garin Port-Harcourt mai arzikin man fetir da ke a yankin kudancin ƙasar. Mutumin wanda aka killace ana kuma lura da shi bayan mutuwar wani likitan a cikin watan jiya wanda ya yi hulɗa da shi,ya mutu ne a lokacin da hukumomin Najeriyar ke yin shelar cewar waɗanda ke ɗauke da cutar ba su da yawa.

Sauran mutane guda biyar sun mutu a Lagos ne, kuma yawancinsu jami'an kiwon lafiya ne, kawo yanzu sama da mutane dubu ne suka mutu da cutar a ƙasashen Saliyio da Laberiya da Najeriya da kuma Guinea.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman