1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dan bindigar Christchurch ya amsa laifinsa

Mohammad Nasiru Awal MAB
March 26, 2020

Ba zato ba tsammani dan bindigar da ya hallaka mutum 51 a masallatai biyu a New Zealand a shekarar 2019 ya amsa laifinsa.

https://p.dw.com/p/3a2vY
Christchurch: Brenton Tarrant - Angeklagter
Hoto: picture-alliance/AP/M. Mitchell

A zaman shari'ar da ake yi na kisan gilla a garin Christchurch na kasar New Zealand, ba zato ba tsammani mutumin da ake tuhuma dan kasar Australiya ya amsa laifinsa.

Kamar yadda 'yan sanda suka nunar mutumin ya amsa laifin hallaka mutane 51. A shekarar 2019 aka harbe mutane har lahira a hare-haren da dan bindigar ya kai kan masallatai biyu a Christchurch. Maharin ya dauki bidiyon ta'asar ya kuma wallafa a intanet.

Gabanin ya kai harin dan bindigar mai shekaru 29, ya wallafa kalaman wariya a intanet. Ana kuma zarginsa da aikata ta'addanci.

Yanzu haka ana tsare da shi a wani kurkuku da ke birnin Auckland, mai nisan sama da kilomita 1000 arewa da garin Christchurch.