1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutumin Faransa zai ja ragamar mulki a Mali

August 16, 2013

Tun ba a sanar da sakamakon zaben a hukumance ba shugaban Faransa Francois Hollande ya taya Ibrahim Boubacar Keita murnar lashe zaben da cewa nasara ce ga demokradiyya.

https://p.dw.com/p/19Qzn
ARCHIV - Ex-Ministerpräsident von Mali Ibrahim Boubacar Keita spricht zu seinen Unterstützern in seinem Hauptquartier in Bamako, Mali am 04.05.2013. Am 11.08.2013 findet die Stichwahl zwischen Boubacar Keïta und Ex-Finanzminister Cissé statt. Foto: EPA/TANYA BINDRA +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

A wannan makon jaridun na Jamus sun fi mayar da hankali ne a kan sakamakon zagaye na biyu na zaben shugaban kasar Mali. A sharhin da ta rubuta mai taken sabon babi da tsoffin fuskoki jaridar Die Tageszeitung cewa ta yi:

"Mali ta samu sabon shugaban kasa wanda zai ja ragamar aikin ceto kasar daga rikice-rikicen da take fama da su. Ibrahim Boukacar Keita wanda 'yan kasar Mali ke kiransa IBK, ya lashe zaben shugabancin kasar bayan yayi takara sau uku. Ko shakka babu zaben Ibrahim Boubacar Keita a matsayin shugaban Mali tamkar wani wakilin tsohuwar gamnatin kasar aka zaba. Sai dai idan aka kwatanta shi da sauran 'yan siyasar kasar ana iya cewa mutum ne mai kamanta gaskiya. Ko da yake a lokacin da ya rike mukamin Firaminista daga shekarar 1999 zuwa 2000, ya azurta kansa, amma ga al'ummar kasar, bai kai abokin hamaiyarsa Souma'ila Cisse dake zaman tsohon ministan kudin kasar, wasashe dukiyar talakawa ba."

France's President Francois Hollande (C), flanked by French Foreign Affairs Minister Laurent Fabius (Back-3rdL) and French Defence Minister Jean-Yves Le Drian (Back-2ndL) shakes hands with Prefects of Mopti upon his arrival at Sevare, near Mopti, on February 2, 2013. President Francois Hollande visits Mali as French-led troops work to secure the last Islamist stronghold in the north after a lightning offensive against the extremists. Hollande will head to Timbucktu and Bamako. AFP PHOTO / PASCAL GUYOT (Photo credit should read PASCAL GUYOT/AFP/Getty Images)
Francois Hollande lokacin wata ziyara a MaliHoto: Pascal Guyot/AFP/Getty Images

Ita kuwa jaridar Berliner Zeitung a lokacin da take sharhi kan kasar ta Mali cewa ta yi mutumin da Faransa ke goya wa baya zai ja ragamar shugabancin Mali, sannan sai ta ci gaba kamar haka:

Zaben Mali nasara ga demokradiyya

"Masu sa ido a zabe na kasashen yamma sun yaba da yadda aka gudanar da zaben shugaban kasar Mali, wadda kawo yanzu ta yi ta fama da tashe-tashen hankulan masu kaifin kishin addini. Tun ba a sanar da sakamakon zaben a hukumance ba shugaban Faransa Francois Hollande ya taya Ibrahim Boubacar Keita dake zama mutumin da Faransa ke marawa baya, murnar lashe zaben da cewa nasara ce ga demokradiyya kuma Faransa za ta dafa masa baya. Shi dai Keita a Faransa yayi karatun jami'a har ma kuma ya koyar. Wani kamfanin hulda da jama'a na Faransa ya jagoranci yakin neman zabensa."

Ayyukan 'yan bindiga a arewacin Najeriya

A residents peers through the shattered widow of a badly-damaged car at the scene of an explosion targeting an open-air beer garden at Enugu Road in the downtown Sabon Gari neighbourhood of the city on July 30, 2013 in Kano. The death toll from a series of bomb blasts that rocked a mainly Christian area of northern Nigeria's largest city of Kano late on July 29 has risen to 12, the military said today, blaming Islamist group Boko Haram for the attacks. The statement blamed the attack on suspected Boko Haram members and said packages that caused the explosions were left in the mainly Christian Sabon Gari area of Kano. AFP PHOTO / AMINU ABUBAKAR (Photo credit should read AMINU ABUBAKAR/AFP/Getty Images) Erstellt am: 30 Jul 2013 Editorial-Bild-Nummer: 175046207 Beschränkungen: Bei kommerzieller Verwendung sowie für verkaufsfördernde Zwecke kontaktieren Sie bitte Ihr lokales Büro. Vollständige redaktionelle Rechte in Großbritannien, USA, Irland, Italien, Spanien, Kanada (außer Quebec). Eingeschränkte redaktionelle Rechte in allen anderen Ländern. Wenden Sie sich bitte an Ihr lokales Büro. Lizenztyp: Lizenzpflichtig Fotograf: AFP/Freier Fotograf Kollektion: AFP Bildnachweis: AFP/Getty Images Max. Dateigröße/ Abmessungen/ dpi: 12,1 MB - 2371 x 1778 Pixel (83,64 x 62,72 cm) - 72 dpi Die Dateigröße für den Download weicht u. U. von den Angaben ab. Quelle: AFP Releaseangaben: Kein Release verfügbar. Weitere Informationen Strichcode: AFP Objektname: Par7627280 Urheberrecht: 2013 AFP Suchbegriffe: Stadt, Zerbrochen, Konflikt, Horizontal, Im Freien, Wohnviertel, Bier, Nigeria, Sehen, Explodieren, Auto, Gewalt, Stadtzentrum, Witwe, Angriff mit Bombe, Eigenheim, Kano - Nigeria, Terrorismus.
Ayyukan 'yan bindiga ya ki ci ya ki cinyewa a NajeriyaHoto: AMINU ABUBAKAR/AFP/Getty Images

Mutane da yawa sun rasu a wani hari da aka kan kan masallaci a Najeriya, inji jaridar Frankfurter Allegemeine Zeitung tana mai sharhi a kan harin da jami'an tsaron Najeriya suka dora laifinsa a kan kungiyar nan da ake wa lakabi da Boko Haram, sannan sai ta ce:

"Jaridun Najeriya dai sun ce wannan harin na da alaka da karuwar kungiyoyin matasa masu kare kai daga 'yan Boko Haram, domin harin yayi kama da wanda aka kai a kan 'ya'yan kungiyoyin kare kai a jihar Borno a tsakiyar watan Yuni da ya gabata inda aka kashe mutane 25. A cikin watannin bayan nan dai an horas da matasa da yawa dubarun yadda za su kare kauyukansu daga hare-haren masu kishin addini tare da rage kaifin mayakan Boko Haram. Sojojin Najeriya ke ba wa wadannan kungiyoyin kare kai makamai. Sai dai duk da tsauraran matakan tsaro da aka dauka da kuma dokar ta-baci da aka kafa a jihohin Borno, Yobe da Adamawa cikin watan Mayu, babu wani lahani na a zo a gani da aka yi wa kungiyar ta Boko Haram, domin har yanzu tana iya kai hari a inda ta so da kuma lokacin da ta so ba tare da shakkan kowa ba."

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Usman Shehu Usman