1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: An dakatar da shirin RUGA

Ahmed Salisu
July 3, 2019

Bayan share tsawon kwanaki ana kace-nace kan shirin nan na RUGA a Najeriya wanda ya tanadi tsugunar da Fulani makiyaya a waje guda da ake son aiwatarwa, gwamnatin kasar ta sanar da dakatar da shirin.

https://p.dw.com/p/3LXaQ
DW Fulani
Hoto: DW/K. Gänsler

Gwamnatin ta Najeriya ta ce ta dau matakin dakatar da shirin saboda irin cece-kucen da ake yi a kai. A wani zama da kwamitin nan na wadata kasar da abinci ya yi a Abuja, mukaddashin kwamitin kuma gwamnan jihar Kebbi Atiku Bagudu ya ce, Shugaban kasar Muhammadu Buhari ne ya bada umarnin dakatar da shirin na RUGA. Ya bukaci da a sake duba shi da nufin yi masa gyaran da ya kamata, ta yadda wandada za su amfana da shirin za su ci moriyarsa sosai, sannan a kawar da duk wani abu daga cikinsa da ka iya jawo fitina a kasar.